Site icon Liberty TV/Radio Hausa – Labaru – Tashar 'Yanci!

Ana Ci Gaba Da Jigilar Maniyyatan Najeriya Zuwa Sa’udiyya

Pilgrims heading for Hajj4

Pilgrims heading for Hajj4

NAHCON na ci gaba da jigilar maniyyatan zuwa ƙasa mai tsarki domin sauke farali a bana.

Ta wallafa a shafinta na X, zuwa yau Asabar da safe jirage 12 ne ɗauke da maniyyatan suka isa Saudiyya.

Hukumar ta ce 11 daga cikin jiragen sun sauka ne a birnin Madina, yayin da ɗaya kuma ya sauka a Jedda.

NAHCON ta ce daga cikin adadin Da suka isa ƙasa mai tsarkin 2934 maza ne, yayin da 2140 mata ne.

A makon nan NAHCON ta fara jigilar maniyyatan, inda aka fara da jihohin Kebbi,Bauchi,Nasarawa,Legos da Abuja.

Exit mobile version