Hukumomin Saudiyya sun kama wani ɗan Nijeriya da wasu
‘yan kasar uku, bisa zargin safarar hodar ibilis da ta kai
nauyin kilogiram 2.2.
Sashen binciken manyan laifuffuka na rundunar ‘yan sanda ta ƙasar, ya ce ya samu nasarar daƙile yunƙurin shigar da hodar ibilis zuwa biranen Riyadh da Jeddah.
‘Yan sandan sun ce, mutanen huɗu sun daɗe su na aikata laifin safarar hodar ibilis, tare da saida ta a cikin ƙasar ta hanyar amfani da wasu miyagun dabaru.
Jami’an ‘yan sandan sun ce, za a gurfanar da mutanen a gaban kotu da zarar sun kammala gudanar da bincike.














































