Gwamnan jihar Kaduna Nasiru El-Rufai, ya bada umarnin biyan kusan malaman firamare dubu 8 da 500 daga cikin dubu 39 da gwamnatin jihar ta dauka aiki basussukan da su ke bi a cikin makon nan.
A cikin wata sanarwa da mai ba gwamnan shawara na musamman a kan yada labarai Muyiwa Adekeye ya fitar, gwamnan ya nuna rashin jin dadin sa a kan yadda kananan hukumomi su ka rike wa malaman makarantar hakkokin su.
Hakan kuwa, ya faru ne da sabbin malaman makarantar firamare da aka dauka a rukuni na biyu a jihar Kaduna.
Ya ce bayan bayani daga ma’aikatar kanananan hukumomi da hukumar SUBEB, gwamnatin jihar ta gano cewa kananan hukumomi su na rike da kusan naira miliyan 1 da dubu 800 na albashin malaman makarantar da aka dauka a karo na biyu.
Gwamnan El-Rufa’i dais hi ne gwamna na farko da ya fara biyan ma’aikatan jihar sa sabon karin albashin da shugaba Buhari ya sanya wa hannu bayan samun sahalewar majalisun kasa.














































