Babban Hafsan rundunar sojin sama Air Marshall Isiaka Amao, ya tabbatar wa ‘yan majalisar dattawa cewa lokaci kaɗan ya rage ayyukan ta’addanci su zama tarihi a Nijeriya.
Air Marshall Amao ya bada tabbacin ne, kwanaki uku kacal bayan mayakan ISWAP sun kashe Janar na sojojin ƙasa a Askira Uba da ke jihar Borno.
Kwamitin sojin sama na majalisar dattawa, ya bukaci rundunar sojin ta ƙara ƙaimi a yakin da su ke yi, domin tabbatar da zaman lafiya a wuraren da lamarin ya shafa.
Hafsan sojin ya bayyana haka ne, yayin da ya ke kare kasafin kuɗi na shekara ta 2022 a gaban kwamitin majalisar dattawa, inda ya ce ‘yan ta’adda na shan luguden wuta ta ko ina babu kakkautawa, wanda hakan ke tilasta masu aje makamai.
You must log in to post a comment.