Home Labaru Zamfara: Jiragen Yaki Sun Yi Wa ‘Yan Bindiga Luguden Wuta

Zamfara: Jiragen Yaki Sun Yi Wa ‘Yan Bindiga Luguden Wuta

603
0
Ibikunle Daramola, Kakakin Rundunar sojin Sama Ta Nijeriya
Ibikunle Daramola, Kakakin Rundunar sojin Sama Ta Nijeriya

Rundunar mayakan sojan sama ta Najeriya ta yi amfani da jiragen yaki wajen yi wa ‘yan bindigar ruwan harsasai a mabuyar su dake dazukan jahar Zamfara.

Mai Magana da yawun rundunar, Iya komodo Ibikunle Daramola,  ne ya bayyana haka, ya ce Sojojin sun kai harin ne a karshen makon da ya  gabata bayan samun bayanan sirri dake tabbatar musu da taruwar ‘yan bindiga a mafakarsu.

Ya ci gaba da cewa rundunar ta sake turawa da wani jirgin yakin Najeriya kirar Alpha Jet zuwa wani gida da ‘yan bindigar suka fake a ciki, inda jirgin ya kona gidan gaba daya ta hanyar jefa masa bama-bamai, wanda hakan ya yi sanadiyyar mutuwar yan bindiga da dama. Cikin wani bidiyo da rundunar ta yada a kafafen sadarwa, an hangi yadda jiragen yaki sun halaka wasu yan bindiga da suke tserewa a kafa suna neman mafaka, wasu kuma aka bi su kauyen Wanoke kafin daga bisani aka hallaka su.