Home Labaru Zamani Ya Juyo Da Mataimakin Gwamna Ya Koma Sakataren Gwamnati Bayan Shekaru

Zamani Ya Juyo Da Mataimakin Gwamna Ya Koma Sakataren Gwamnati Bayan Shekaru

154
0

Gwamnan jihar Katsina Dikko Umaru Radda, ya amince da
nadin Abdullahi Garba Faskari a matsayin sakataren
gwamnatin jihar.

Babban mai taimaka wa Gwamnan a kafofin sadarwa na zamani Isah Miqdad ya wallafa sanarwar a shafin sa na Facebook, inda ya ce Abdullahi Garba Faskari ne zai canji Ahmed Musa Dangiwa, wanda zai zama Minista a gwamnatin shugaba Bola Ahmed Tinubu.

A Tsakanin shekara ta 2011 da 2015 dai, Abdullahi Garba Faskari ne Mataimakin Gwamnan jihar Katsina a lokacin mulkin Ibrahim Shehu Shema.

Mutane da dama dai sun yi mamakin jin yadda tsohon Mataimakin Gwamnan zai zama sakatare.

Leave a Reply