Gamayyar kungiyoyin Arewacin Najeriya, ta nuna adawarta ga tsarin karba-karba da jam’iyyun siyasa suke kawo wa yayin da ake shirin zabe.
Mai magana da yawun kungiyar Abdul-Azeez Suleiman, ya bayyana cewa wannan tsarin ya saba dokar kasa, kuma yunkuri ne na murkushe ‘yan Arewa.
A wajen taron manema labarai Abdul-Azeez Suleiman, ya ce an kawo wannan batu ne da nufin a hana Arewa takara a zaben 2023.
Suleiman ya yi kira ga jam’iyyun siyasar kasar nan su yi watsi da maganar karba-karba da kuma kai tikitin takarar shugaban kasa zuwa kudancin kasar nan a 2023.
Ya ce Gamayyar kungiyoyi 60 a karkashin ta, ta na so duk jam’iyyu su yi koyi da gwamnonin Arewa da suka dauki matsayar cewa karba-karba ya saba doka.
A cewar sa, mutanen Arewa ba za su yarda da wani shiri na hana su neman kujera a zabe mai zuwa ba.
You must log in to post a comment.