Home Labaru Yaki Da Rashawa: Buhari Ya Na Farin Ciki A Kan Samun Nasarar...

Yaki Da Rashawa: Buhari Ya Na Farin Ciki A Kan Samun Nasarar – Malami

346
0
Abubakar Malami, Tsohon Ministan Shari'a Na Najeriya,
Abubakar Malami, Ministan Shari'a Na Najeriya,

Ministan Shari’a na Najeriya, Abubakar Malami, ya ce shugaban kasa Muhammadu Buhari ya yi farin ciki kan samun nasarorin gwamnatinsa wajen dawo da dukiyar kasa.

Malami, ya bayyana hakan ne a yayin bikin bayar da kyaututtuka na shekarar bara da aka gudanar a ma’aikatar shari’a ta kasa dake Abuja.

Abubakar Malami wanda ya sami wakilcin mai Magana da yawunsa Salihu Othman Isah, ya ce ma’aikatar shari’a ta taka mataki na samun nasarori musamman a bangaren yaki da rashawa tare da wasu muhimman ababe na matse lalitar gwamnati gami da kwazon ta wajen rage cunkoso a gidajen yari. Ministan, ya bayyana yadda ma’aikatar sa ta yi kwazo wajen dawo da dukiyar kasa da gwamnatocin baya suka  sace, tare da jajircewa wajen shimfida ingantattun tsare-tsare.