Shugabannin kasashen kungiyar yankin Sahara sun gudanar da wani taron gaggawa a Chadi wanda ya mayar da hankali akan rikicin kasar Sudan .
Shugaban Chadi Idris Deby Itno, ya bayyana damuwa matuka da cewa yanayin da wasu kasashe ke dab da fadawa kan iya haifar da wani sabon rikici a kan iyakokin kasashen su.
Ya ce a kasar Sudan jam’iyyar NCP ta tsohon shugaban kasar Omar El Beshir , ta kalubalanci juyin mulki da sojojin kasar suka yi, ta kuma bukaci ganin an sako ilahirin shugabanin ta dake tsare yanzu haka. A karshe jam’iyyar a wata sanarwa da ta fitar na nuni cewa kwace mulki ta hanyar kifar da gwamnati ya sabawa kudin tsarin mulki wanda hakan ke da babban hadari.
You must log in to post a comment.