’Yan bindiga sun nemi a biya su kudin fansa da sabbin takardun Naira bayan sun yi garkuwa da mutum 46 a a kauyukan kananan hukumomin Funtua da Batsari na Jihar Katsina.
Da safiyar ranar Juma’ar da ta gabata ne Maharan kusan su 40 a kan babura, suka kashe mutum daya, tareda sace wasu 28, ciki har da mata da kananan yara a kauyen Karare da ke Karamar Hukumar Batsari.
Bayanai sunce “Daga cikin wadanda aka sace harda wasu dalibai daga kauyen Kokiya da ke hanyarsu ta zuwa Makarantar Sakandaren Je-ka-ka-dawo a kauyen.
Wani mazaunin garin ya ce yana asibiti lokacin da aka kai harin, amma ya tsallaka katanga ya tsere.
A daya harin kuma, ’yan bindiga sun far wa wani masallaci a kauyen Maigamji da ke kan Babbar Hanyar Funtua zuwa Dandume, inda suka bude wuta kan masu Sallar Isha’i.
Wani Ganau yace a yayin harin maharan sun harbi limamin da ke jan sallar da wani mutum daya, sannan suka sace mutum 18 daga masallacin a ranar Asabar.
Mai magana da yawun ’yan sanda na Jihar Katsina, SP Gambo Isa, yace suna gudanar da bincike domin tabbatar da adadin mutanen da abin ya rutsa da su.














































