Home Labaru Labarun Ketare Sojoji Sudan Sun Ce Sun Ƙwace Iko Da Wasu Sassan Khartoum Daga...

Sojoji Sudan Sun Ce Sun Ƙwace Iko Da Wasu Sassan Khartoum Daga Hannun RSF

326
0
bd87693e 2fec 41a1 aec1 4dd9dc3403eb cx0 cy3 cw0 w1080 h608
bd87693e 2fec 41a1 aec1 4dd9dc3403eb cx0 cy3 cw0 w1080 h608

Rundunar sojin Sudan ta ce ta ƙwace wasu muhimman wurare a babban birnin ƙasar da kewaye, kwana guda bayan ta kai sabon farmaki kan dakarun RSF.

Sojojin sun bayyana nasarar da suka samu a Khartoum da kuma birnin Bahri, inda suka yi amfani da atilari da hare-hare ta sama da kasa.

A ranar Alhamis shugaban rundunar RSF Janar Hamdan Dagalo ya shaidawa taron MDD cewar ya shirya domin amincewa da tsagaita wuta.

To amma janar Abdel Fattah Al-Burhan ba zai yiwu a cimma yarjejeniyar tsagaita wuta ba har sai RSF sun janye daga yankunan da suka mamaye tun farkon fara yakin basasar.

Leave a Reply