Home Labaru Shi’a: Fadar Shugaban Kasa Ta Ce ‘Yan Sanda Da Sojoji Na Da...

Shi’a: Fadar Shugaban Kasa Ta Ce ‘Yan Sanda Da Sojoji Na Da Ikon Daukar Mataki

419
0

Fadar shugaban kasa ta ce, hukumomin tsaro su na da damar daukar kowane irin mataki a kan kungiyar Shi’a, wadda aka ayyana a matsayin kungiyar ta’addanci kamar yadda su ka dauki mataki a kan kungiyar Biyafara.

Har ila yau, Fadar ta bukaci kungiyar ta shi’a ta yi biyayya ga umurnin babbar kotun tarayya cewa kada su kara fitowa yin zanga-zanga.

Mai taimakawa shugaban kasa ta fuskar yada labarai da hulda da jama’a Garba Shehu ne ya bayyana haka, a cikin shirin Turanci mai suna ‘Sunrise Daily’ da gidan talabijin na Channels ke gabatarwa.

Mai taimakawa shugaban kasa ta fuskar yada labarai da hulda da jama’a Garba Shehu

Yayin da ya ke amsa tambayoyi, Garba Shehu ya ce a Kaduna lamarin ya yi tasiri, domin an samu nasarar dakile gangamin  haddasa tashin hankali