Home Labaru Martani: Babu Ma’aikacin Da Ke Bin Gwamnatin Kogi Bashin Albashi – Yaha...

Martani: Babu Ma’aikacin Da Ke Bin Gwamnatin Kogi Bashin Albashi – Yaha Bello

458
0
Yahaya Bello, Gwamnan Jihar Kogi

Gwamnan jihar Kogi Yahaya Bello, ya ce Shugaba Muhammadu Buhari ya ba shi tallafi na kimanin naira biliyan 30 da miliyan 8 domin biyan bashin albashin ma’aikatan jihar.

Yahaya Bello dage a kan cewa a halin yanzu ba a bin gwamnatin sa bashin albashi domin ta na biyan ma’aikata duk wata.

Gwamnan ya bayyana wa manema labarai haka ne, bayan ganawar da ya yi da kwamitin Jam’iyyar APC na kasa, da wadanda su ka yi takarar zaben fidda gwani na kujerar gwamnan jihar Kogi a zabe mai zuwa.

Dangane da labaran da ake yadawa cewa ma’aikata na bin jihar Kogi bashin albashi, ya ce matsala ce da ya gada a lokacin da ya hau mulki, amma a halin yanzu ma’aikata basu bin jihar Kogi bashin albashi.

Leave a Reply