Home Coronavirus Kotu Ta Yi Wa Dattijon Da Ya zagi Buhari Da Masari Hukunci...

Kotu Ta Yi Wa Dattijon Da Ya zagi Buhari Da Masari Hukunci daurin watanni 18

4118
0
Kotu Ta Yi Wa Dattijon Da Ya zagi Buhari Da Masari Hukunci daurin watanni 18
Kotu Ta Yi Wa Dattijon Da Ya zagi Buhari Da Masari Hukunci daurin watanni 18

Wata kotu a jihar Katsina ta yanke wa wani mutum mai shekaru 70 mai suna Lawal Abdullahi Izala hukuncin daurin watanni 18 a gidan gyaran hali.

An dai kama Izala ne bisa zargin sa da zagin shugaban kasa Muhammadu Buhari da Gwamnan jihar Katsina Aminu Masari a makon da ya gabata.

Wata majiya ta ce, an gurfanar da Lawal Abdullahi da wasu mutane biyu a gaban kuliya a kan tuhumar su da furta kalaman da za su iya tada zaune tsaye.

Da ya ke zantawa da manema labarai,  Izala ya ce ya yi furucin ne a cikin fushi a lokacin da ya ziyarci kauyen su ya gano cewa ‘yan bindiga sun kashe wasu yan uwan sa sun kuma sace shanu 15.

A yayin zartar da hukuncin, alkalin kotun ya ce an samu Izala da laifukan assasa fitina da rashin da a ga hukuma, matakin da ya sa aka yanke masa hukuncin daurin watanni shida a gidan gyaran hali a laifin farko, sai kuma na shekara guda na laifi na biyu.

A karshe alkalin ya ba Izala zabin biyan tara ta naira dubu 10 a laifin farko, da kuma naira dubu 20 a laifin na biyu, sai dai wasu mutane a jihar sun biya wa dattijon kudin tarar, lamarin da ya sa alkalin ya sake shi.