An gano karin wasu mutum biyu da suka kamu da cutar coronavirus wadda aka samu bullarta a jiha biyar a fadin Najeriya.
Da hakan ne adadin wadanda suka kamu cutar ya karu zuwa 42 a kasar, a cewar Hukumar Hana Yaduwar Cututtuka (NCDC), a ranar Talata.
Hukumar ta bayyana cewa an samu karin masu dauke da coronavirus ne a jihohin Legas da Ogun.
Ta kara da cewa zuwa yanzu cutar ta bazu a Jihohin Legas, Ogun, Oyo, Ekiti, Edo da kuma Babban Birnin Tarayya Abuja.
Mutum 29 ne suka kamu da cutar a jihar Legas sai kuma mutum 7 a Abuja. Akwai kuma mutum 3 a Ekiti; 1 a Oyo da wani 1 a jihar