Jam’iyyar NNPP, ta ce dan takarar ta na shugaban kasa Sanata Rabi’u Musa Kwankwaso, ya zabi Bishop Isaac Idahosa daga jihar Edo a matsayin abokin takarar sa a zaben shekara ta 2023.
Bishop Isaac Idahosa dai babban Fasto ne a cocin God First Ministry da ke da helkwata a jihar Legas.
Zaben faston dai ya na zuwa ne, bayan rade-radin da ke cewa Kwankwaso ya na neman zaben tsohon gwamnan jihar Anambra Peter Obi a matsayin abokin takarar sa.