Wani jami’in Hukumar Yaki da cin hanci da rashawa EFCC,
ya rasa ran sa a wani fada da ya barke tsakanin shi da abokan
aikin sa a Jihar Sokoto.
Kakakin hukumar EFCC Wilson Uwujaren, ya ce wasu jami’an hukumar uku sun kaure da fada ne bayan takaddama ta barke tsakanin su a kan ajiyar wasu kaya.
Ya ce likitocin Asibitin Koyarwa na Jami’ar Danfodio da ke Sokoto ne su ka tabbatar da rasuwar jami’in mai suna Sufeto Abel Isah Dickson a ranar 7 ga watan Mayu.
Uwujaren, ya ce tuni sauran mutane biyun su na tsare a hannun ‘yan sanda bayan faruwar lamarin.














































