Home Labaru Idan Tinubu Ya Zama Shugaban Kasa Zan Bar Nijeriya – Bode George

Idan Tinubu Ya Zama Shugaban Kasa Zan Bar Nijeriya – Bode George

192
0

Tsohon Gwamnan jihar Ondo Cif Bode George, ya lashi takobin cewa idan har Bola Tinubu ya zama Shugaban kasa zai kwashe kayan sa ya bar Nijeriya kwata-kwata.

Bode George ya bayyana haka ne, a wata tattaunawa da yay i da jaridar Vanguard, inda ya ce Tinubu ba irin mutumin da za a mika wa mulkin Nijeriya ba ne domin kashe ta zai yi.

Ya ce Tinubu ba irin mutumin da za a damka wa amanar babbar kasa kamar Nijeriya ba ne, don haka kamata jama’a su su maida hankali a kan wanda zai jagorance su.

Bode George ya kara da cewa, mutanen da ke goyon bayan Tinubu kawai wadanda ke amfana da kudin sa ne.

Leave a Reply