Gwamna Babagana Umara Zulum na jihar Borno, ya kaddamar da shafin yanar gizo da za a dauki ma’aikata kimanin miliyan biyu daga sassan daban-daban na jihar aiki.
Kwamishinan ma’aikatar kimiyya da fasaha na jihar Babagana Mustapha ne ya kaddamar shafin a birnin Maiduguri na jihar Borno.
Babagana Mustapha, ya ce an kirkiri shafin ne saboda tattara bayyanan wadanda za a dauka aikin koyarwa da sauran kwararru a ma’aikatun da ake neman masu aiki.
A
na shi bangaren, gwamna Zulum ya yi kira ga ma’aikatar ta yi hadin-gwiwa da ma’aikatun
ilimi da sadarwa, domin inganta samar da ingancin yanar gizo ga masu neman aiki
a jihar.