FEMA, ta tabbatar cewa ba a samu asarar rai ba bayan rugujewar da wani gini mai hawa huɗu a r Garki.
A cewar mai riƙon muƙamin shugabar hukumar, Florence Wenegieme, ginin da haɗarin ya shafa, ana yi masa gyare-gyare ne.
Shaidu sun ce galibin ma’aikatan da ke aiki a wajen sun tashi aiki lokacin da lamarin ya faru.
hukumar ta zargi ɗan kwangilar da ke aiki a ginin saboda yin burus da umarnin da hukumomi suka ba shi na ya dakatar da aiki kan ginin.
A cewar hukumar, an kuɓutar da mutum uku da suka samu rauni kuma tuni aka sallame su daga asibiti.














































