Kungiyar ‘yan wasan Najeriya Super Eagles ta bayyana dalilin da ya sa ba a kira dan wasan Leicester City Ademola Lookman ba a cikin tawagar ‘yan wasan na Najeriya.
A makon da ya gabata kungiyar ta fitar da jerin ‘yan wasa 28 da za su wakilce ta a gasar cin kofin nahiyar Afirka ta AFCON da za a fara wannan wata a Kamaru.
Sai dai babu sunan Lookman a cikin, wanda dan wasan Leicester City ne a gasar Premier League ta Ingila, lamarin da ya janyo suka daga wasu ‘yan Najeriya.
Sai dai cikin wata sanarwa da ta fitar a karshen makon da ya gabata, Super Eagles ta ce har yanzu hukumar kwallon kafa ta FIFA ba ta kammala tantance dan wasan ba.
You must log in to post a comment.