Tsohon ministan Sadarwa Adebayo Shittu, ya ce ya yi matukar mamaki da ya ga babu sunan sa a jerin sunayen ministocin da shugaba Buhari ya nada.
Ya ce ko a mafarki, bai taba tunanin cewa shugaba Muhammadu Buhari ba zai sa sunan sa a jerin sunayen ministocin da ya nada ba.
Tsohon ministan, ya ce ya yi tawakkali ga Allah kuma ya yarda da hukuncin Allah, kuma dole ya gode wa Allah a matsayin sa na Musulmi.
Ya ce yanzu zai koma ya ci-gaba da harkar sa ta aikin lauya, domin tuni ya bude ofisoshin sa a Abuja, kuma zai rungumi kaddara ya cigaba da aikin san a lauya.
Ku biyo mu a shafukanmu na dandalin sada zumunta:
Facebook: https://facebook.com/libertytvnews
Twitter: https://twitter.com/libertytvnews
Instagram: https://instagram.com/libertytvng
Liberty Radio 103.3 FM Abuja Kai Tsaye A Yanar Gizo ??
zeno.fm/libertyradioabuja
Tashar Ƴanci 103.1 FM Kaduna Kai Tsaye A Yanar Gizo ??
zeno.fm/tasharyancikaduna ?
Kira ??? +1-701-719-6971 don suraren (Tashar Ƴanci 103.1 FM Kaduna) kai tsaye ta wayar hannu. Musamman Ga Waɗanda Suke Ƙasar Amurka.
Kuna iya turo mana labari ko shawara a: info@libertytvradio.com














































