Home Labaru Kiwon Lafiya Zazzabi Cizon Sauro: An Fara Rigakafi A Najeriya

Zazzabi Cizon Sauro: An Fara Rigakafi A Najeriya

200
0
image 713 1536x1024 (1)
image 713 1536x1024 (1)

An Fara Rigakafin Zazzabin Cizon Sauro A Nijeriya.

Nijeriya ce kasar dake da kashi 27 cikin 100 na masu dauke da cutar zazzabin cizon sauro a duniya.

Sannna kasar nan na da kuma kashi 31 na wadanda cutar ke kashewa a duniya, kamar yadda rahoton malaria na duniya na 2023 ya nuna.

Akalla mutum 200,000 ne suka rasu a sanadiyar cutar zazzabin cizon sauro a shekarar da ta wuce.

Kazalika, yara ‘yan kasa da shekara biyar da mata masu ciki ne suka fi saurin kamuwa.

Nijeriya ta karbi allurar rigakafin cutar a watan Oktoba, sannan an fara allurar a jihohin Bayelsa da Kebbi.

Daga bisani za a fadada rigakafin zuwa wasu jihohin nan da wasu watanni masu zuwa.

Leave a Reply