Majalisar wakilan Najeriya ta bukaci gwamnatin tarayya ta gaggauta dakatar da yarjejeniyar Samoa da ta tayar da ƙura a kasar.
A zaman da ta yi yau Talata, majalisar ta ce ya kamata a dakatar da yarjejeniyar har sai gwamnati ta fito ta bayyana ɓangarorin yarjejeniyar da suka haifar da cecekuce.
Ɗan majalisar wakilai Hon Aliyu Madaki, ya ce majalisar ta kuma nemi ministocin da suka jagoranci sanya hannu a yarjejeniyar
su gurfana gabanta tare da takardun yarjejeniyar domin buƙatar fayyace komi musamman “ɓangaren dake bayani kan daidaiton jinsi.
Yarjejeniyar Samoa da gwamnatin Najeriya ta sanya wa hannu da tarayyar Turai ta tayar da ƙura a Najeriya inda wasu ƴan ƙasar nan da dama suka nuna fushinsu
musamman zargin cewa yarjejeniyar na ƙunshe da wani ɓangare da ke nuna goyon baya da kuma kare muradun masu maɗigo da luwaɗi.
Sai dai tuni gwamnatin Najeriya ta musanta, inda ministan kasafin kudi da tsare-tsare da kuma ministan watsa
labarai suka ce Najeriya ba za ta taɓa amincewa da wata yarjejeniyar da ta saɓa wa kundin tsarin mulkin ƙasar nan da kuma al’adu da addinin ƙasar.














































