Shugaban ɗariƙar Katolika a yankin Sokoto Bishop Mathew
Hassan Kukah, ya ce ba a taɓa cin rashawa a Nijeriya ba
kamar zamanin mulkin shugaba Muhammadu Buhari.
Bishop Kukah ya bayyana haka ne, yayin da ke jawabi a wajen bikin cikar Babalola shekaru 60 da zama lauya, inda ya ce duk da dai ba a mulkin Buhari aka fara cin rashawa a Nijeriya ba, amma lamarin yafi muni a zamanin sa.
Ya ce a gwamanatin Muhammadu Buhari sun ga mafi nunin cin hanci da rashawa ta fannin tarbiyya da hada-hadar kuɗi da ma fannoni da dama.
Bishop Mathew Kukah, ya kuma koka da yadda shugabanni ke tattare ayyukan ci-gaban al’umma zuwa yankunan da su ka fito, ya na mai cewa hakan ba zai taimaka wajen bunƙasa dimokraɗiyya a Nijeriya ba.














































