Home Home Kungiyar CNG Ya Bukaci EFC Ta Hana Duk Na Kusa Da Buhari...

Kungiyar CNG Ya Bukaci EFC Ta Hana Duk Na Kusa Da Buhari Barin Nijeriya

31
0

Gamayyar Kungiyoyin Arewa CNG, ta bukaci hukumomin yaki da cin hanci da rashawa cewa kada su bar wadanda su ka rike mukami a gwamnatin shugaba Buhari su bar Nijeriya.

Kungiyar dai ta na magana ne, a kan wadanda ake zargi da cin hanci da rashawa a gwamantin da ta ta gabata, musamman gwamnan babban bankin Nijeriya Godswill Emefiele bisa zargin da ake yi masa.

Mai Magana da yawun Kungiyar Abdul-Azeez Suleiman ya bayyana haka yayin wani taro da su ka gudanar, inda kungiyar ta soki masu neman kawo cikas a rantsarwar da aka gudanar a Abuja.

Kungiyar, ta kuma bukaci Hukumar Yaki da Cin Hanci da Rashawa ta kara bincike a kan badakalar da ake yi a ma’aikatu da sauran hukumomin gwamnati domin gurfanar da masu laifi.

Leave a Reply