Home Labaru Kamfanin NNPC Ya Tallafawa ‘Yan Gudun Hijira Dubu 6

Kamfanin NNPC Ya Tallafawa ‘Yan Gudun Hijira Dubu 6

381
0
Kamfanin NNPC
Kamfanin NNPC

Kamfanin man fetur na Najeriya NNPC tare da hadin guiwar ma’aikatar man fetur ta OROTON sun ba ‘yan gudun hijira sama da dubu shida a jihar Adamawa tallafin kayayyaki na dimbin kudi.

Abubakar Yakubu, shugaban sashen lura da barna na kungiyar Red Cross a Najeriya, ya ba da kayayyakin ga ‘yan gudun hijirar da ke Malkohi a karamar hukumar Yola ta kudu a madadin kamfanonin.

Kayayyakin sun hada da kayan abinci da sauran kayayyakin amfanin yau da kullum.

Yace akalla gidaje  1200 ne za su amfana da kayayyakin a tsakanin kananan hukumomi uku a jihar.