Home Labaru Jerin Sunayen Masu Mukamai 10 A Lokacin Buhari Da Ya Kamata Tinubu...

Jerin Sunayen Masu Mukamai 10 A Lokacin Buhari Da Ya Kamata Tinubu Ya Bincika

275
0

Tsohon mataimakin sakataren yaɗa labarai na jam’iyyar APC
na ƙasa Timi Frank, ya buƙaci shugaba Tinubu ya binciki
wasu masu manyan mukamai a tsohuwar gwamnatin
Muhammadu Buhari.

A cikin wata sanarwa da ya fitar, Timi Frank ya ce ya kamata Tinubu ya gudanar da bincike a kan zargin cin zarafin ofishin wasu daga cikin su, kuma kada a bari su guje wa hukunci.

Fimi Frank ya bayyana sunayen ‘yan majalisar ministocin Buhari da ya kamata su kasance a komar Hukumomin EFCC DSS.

Ya ce ya kamata a binciki Timipre Sylva, da Sanata Hadi Sirika da Abubakar Malami da Mele Kyari da Sadiya Umar Farouq da Hadiza Bala Usman Kanar Hammid Ali.

Sauran sun hada da – Babban jami’in Hukumar Kula da Tsaron Ruwa ta Nijeriya Bashir Jamo, da Tsofaffin manajojin daraktoci da shugabannin Hukumar Raya Yankin Neja-Delta NDDC da duk shugabannin tsaron da aka yi wa ritaya cikin kwanakin nan.

Leave a Reply