Home Labaru Kiwon Lafiya Harin Gaza: Ma’Aikatar Lafiyar Hamas Ta Ce Adadin Mutanen Da Aka Kashe...

Harin Gaza: Ma’Aikatar Lafiyar Hamas Ta Ce Adadin Mutanen Da Aka Kashe a Gaza Sun Haura 33,000

56
0
Palestinian fighters from the armed wing of Hamas take part in a military parade to mark the anniversary of the 2014 war with Israel, near the border in the central Gaza Strip, July 19, 2023. REUTERS/Ibraheem Abu Mustafa

Ma’aikatar lafiya ta Hamas ta ce adadin mutanen da aka kashe a Gaza tun daga ranar 7 ga Oktoba ya ƙaru zuwa dubu 33 da 37.

Adadin wadanda suka mutu ya hada da mutuwar mutane 62 a cikin awanni 24 da suka gabata.

Sanarwar ma’aikatar ta ƙara da cewa adadin mutanen da suka jikkata tun ranar 7 ga Oktoba ya kai dubu 75 da 668.

Sojojin Isra’ila sun fara kai farmakin ne bayan harin na ranar 7 ga watan Oktoba da mayaƙan Hamas suka kai inda suka kashe kimanin mutanen Isra’ila 1,200.

Leave a Reply