Home Labarai Albashi: NLC Ta Sake Yin Fatali Da Bada Naira Dubu 54

Albashi: NLC Ta Sake Yin Fatali Da Bada Naira Dubu 54

242
0
Nigeria Labour Congress logo.svg (1)
Nigeria Labour Congress logo.svg (1)

ƙungiyoyin ƙwadago na Najeriya sun sake yin fatali da tayin mafi ƙarancin albashi na naira 54,000 da gwamnatin tarayya ta ce za ta biya.

A tataunawar da ƙungiyar ta yi da kwamitin ƙarin albashi da gwamnatin Najeriya ta kafa,

Hakan ƙari ne a kan naira 48,000 da kwamitin gwamnatin tarayyar ya yi tayin biya a zaman da ɓangarorin biyu suka yi cikin makon da ya gabata.

Sai dai kuma NLC ta ce ta yi watsi da tayin ne sakamakon halin matsin rayuwa da ake fuskanta a ƙasar.

A halin da ake ciki dai ɓangarorin biyu za su sake zama a yau Laraba domin ci gaba da tattaunawar kan mafi ƙarancin albashin.

Tun da farko dai NLC ta ce tana so gwamnatin ta biya naira 615,000 ne a matsayin mafi ƙarancin albashi,

la’akari da halin da ake ciki a ƙasa na ƙaruwar hauhawar farashi da karyewar darajar Naira.

Leave a Reply