Site icon Liberty TV/Radio Hausa – Labaru – Tashar 'Yanci!

Gurfana Gaban Kwamiti: Zailani Ya Ce Majalisa Ƙarƙashin Sa Ba Ta Amince Wa El-Rufai Ya Karɓo Bashi Ba

img 20210227 wa0004 2

img 20210227 wa0004 2

Tsohon shugaban majalisar dokokin jihar Kaduna Yusuf Zailani ya bayyana cewa majalisar Kaduna a karkashin sa ba ta amincewa wa tsohon gwamnan jihar Nasir El-Rufai ya ciwo bashi daga waje ba.

Sabon shugaban majalisar jihar, Yusuf Liman ne ya kafa wata kwamiti domin ta binciki yadda gwamnatin El-Rufai ya ciwo bashin dala miliyan 350, yadda ta kashe su da kuma kwangilolin da ta yi a lokacin mulkin sa.

Kwamitin za ta gayyaci tsohon kwamishinan kuɗi Mohammed Sani Dattijo da kuma wasu jigajigan gwamnatin Kaduna a lokacin gwamnatin El-Rufai.

Sai dai kuma tsohon shugaban Majalisar jihar, Yusuf Zailani wanda a baya makusancin El-Rufai ne ya wanke kan sa daga zargin shine ya saka wa tsohon gwamnan jihar hannu ya ciwo bashin..

Zailani ya ce  ko da El-Rufai ya buƙaci su bashi dama ya ciwo bashin dala miliyan 350, ya ki saka mishi hannu amma ya yi gaban kan sa.

Zailani ya ce yana da shaidu har yanzu a majalisar wanda sun san da haka.

Exit mobile version