Hukumar bada agajin gaggawa ta Najeriya ta ce adadin waɗanda suka rasu a sanadiyar fashewar tankar mai a jihar Jigawa ya kai 147, sannan kusan 90 suna asibiti.
Lamarin wanda ya auku da tsakar daren Talata, ya yi muni ne saboda mutane da dama sun zo wurin ɗibar man da ke zuba daga cikin motar bayan ta faɗi.
An samu ƙaruwar waɗanda suka rasu ne daga cikin waɗanda suke kwance suna jinya a asibiti, bayan an yi wa wasu jana’iza.