Ma’aikatar Lafiya ta Jihar Kano ta tabbatar da karuwar mutum 5 da ke dauke da cutar coronavirus a jihar.
Sanarwar da Ma’aikatar ta fitar a ranar Laraba ta ce sabbin mutum 5 da ke dauke da cutar sun yi alaka da wanda ya fara kamuwa da cutar.
Kawo yanzu mutum 9 ne suka kamu da annobar coronavirus a jihar Kano.
A ranar Laraba, 14 ga watan Afrilun da muke ciki ma an samu karin mutum 1 da ya kamu da cutar, kamar yadda ma’ikatar lafiayr ta tabbtar.
Karuwar masu cutar a jihar ta sa Gamna Abdullahi Ganduje sanya dokar hana zirga-zirga na tsawon sa’a 24 a fadin jihar, a matakin farko.
Gwamnan ya sanar da haka ne a lokacin taron da ya yi da malaman addini kan annobar cutar a ranar Laraba.