Yawan mutanen da suka kamu da cutar coronavirus a Jihar Kano ya sake karuwa a ranar Talata.
Ma’aikatar Lafiya ta Jihar Kano ta tabbatar da kamuwar mutum na 4 da cutar a jihar, bayan fitowar sakamakon gwajin da aka yi masa.
Gwamnatin jihar ta ce mutum na 4 da ya kamu da cutar ya samu kusanci da wanda ya fara harbuwa da cutar a jihar Kano.