Site icon Liberty TV/Radio Hausa – Labaru – Tashar 'Yanci!

‘Yan Sanda 10,000 Da Aka Yaye Za Su Yi Aiki Lokacin Zaben Najeriya Na 2023

Shugaban rundunar ‘yan sandan Nijeriya Usman Alkali Baba, ya ce sabbin kananan jami’an ‘yan sanda dubu 10 da aka yaye kwanan nan, za a tura su zuwa sassan Nijeriya domin tabbatar da doka da oda lokacin zaben shekara ta 2023.

Shugaban rundunar ‘yan sandan Nijeriya Usman Alkali Baba, ya ce sabbin kananan jami’an ‘yan sanda dubu 10 da aka yaye kwanan nan, za a tura su zuwa sassan Nijeriya domin tabbatar da doka da oda lokacin zaben shekara ta 2023.

Mataimakin shugaban ‘yan sandan Nijeriya mai kula da shiyya ta 8 Ashafa Adekunle ya bayyana haka, a wajen bikin yaye daliban makarantar horon ‘yan sanda da ke Ilori a matsayin wakilin Usman Alkali Baba.

Adekunle, ya ce bayan faretin kammala horar da sabbin ‘yan sandan, za a tura su zuwa sassan Nijeriya lokacin zabubbukan shekara ta 2023, inda za su yi aikin tabbatar da tsaro domin a gudanar da sahihin zabe cikin kwanciyar hankali da lumana.

Yayin da zaben shekara ta 2023 ke kara karatowa, ana nuna damuwa a kan sha’’anin tsaro da ke kara tabarbarewa a wasu sassan Nijeriya, musamman yankin arewacin Nijeriya da ake fama da ‘yan bindiga.

Exit mobile version