Site icon Liberty TV/Radio Hausa – Labaru – Tashar 'Yanci!

Kiwon Dabbobi: Tinubu Ya Kirkiro Sabuwar Ma’aikatar Tarayya,

Baba Usman Ngelzarma

Baba Usman Ngelzarma

Shugaba Bola Tinubu ya bayar da umarnin kirkirar sabuwar ma’aikatar tarayya da za a rika kira da ‘Ma’aikatar Raya Dabbobi’.

An sanar da kirkirar ma’aikatar ne yayin kaddamar da kwamitin aiwatar da gyara kan harkokin kiwon dabbobi domin magance rikicin manoma.

Kungiyar Fulani ta Miyetti Allah (MACBAN) ta bukaci shugaban kasa Bola Tinubu da ya samar da ma’aikatar kiwon dabbobi.

Alhaji Baba Usman Ngelzarma, shugaban kungiyar ta MACBAN ne ya yi wannan kiran a watan da ya gabata,

inda ya ce makiyaya na neman a samar masu da ma’aikatar bunkasa kiwo.

Exit mobile version