Gwamnatin tarayya ta ce ta bankado ma’aikatan da aka dauka
aiki da takardun bogi guda dubu 1 da 618.
Shugaban ma’aikatan tarayya Folashade Yemi-Esan ta bayyana haka, a wani taron manema labarai kafin gudanar da makon ma’aikata na shekara ta 2023.
Folashade, ta ce gwamnatin tarayya ta bankado ma’aikatan ne a cikin tsarin biyan albashi na IPPIS.
Ta ce an kuma gano wasu ma’aikata dubu 69 da 854 a wasu manyan ma’aikatun gwamnatin tarayya da hukumomin gwamnatin tarayya da ke shiyyoyi shida na Nijeriya da birinin tarayya Abuja.
Folashade Yemi-Esan ta kara da cewa, bisa aikin da ake ci- gaba da gudanarwa, an dakatar da wasu ma’aikatan daga cikin tsarin albashi na IPPIS.

