Site icon Liberty TV/Radio Hausa – Labaru – Tashar 'Yanci!

Gwamnatin Kaduna Ta Kara Makonni Biyu Na Dokar Kulle

Gwamnatin Kaduna Ta Kara Makonni Biyu Na Dokar Kulle

Gwamnatin Kaduna Ta Kara Makonni Biyu Na Dokar Kulle

Gwamnatin jihar Kaduna ta tsawaita dokar hana zirga-zirga na tsawon makonnin biyu domin dakile yaduwar cutar Coronavirus a fadin jihar.

Gwamnan jihar Nasiru El-Rufai ya sanar da haka ta bakin mataimakiyar sa Hadiza Balarabe, tare da cewa an tsawaita dokar ne biyo bayan shawarwarin kwararru a kan harkokin lafiya, a dai-dai lokacin da aka kwashe kwanaki 60 da cikin dokar.

Hadiza ta ce, kara wa’adin dokar bai rasa nasaba da irin karin shirye-shirye da jihar ke yi na sake bude harkokin yau da kullum, da kuma bada cikakkiyar kariya ga al’ummar jihar.

A karshe mataimakiyar gwamnan ta kara da cewa, makarantu da wuraren ibada da kasuwanni za su ci gaba da kasancewa a rufe, yayin da za a rika tattaunawa da malamai da jami’an gwamnati da masarautun gargajiya da kungiyoyin sufuri da sauran su.

Exit mobile version