Shugaban kasa Muhammadu Buhari, ya bukaci Majalisar
Dattawa ta amince ya ciyo bashin Dala miliyan 800.
Buhari ya gabatar da bukatar ne a cikin wata wasika da ya aike wa shugaban majalisar Dattawa Sanata Ahmad Lawan, wadda ya karanta a wani zama da ‘yan majalisar suka yi a ranar Talatar da ta gabata.
A cikin wasikar, shugaba Buhari ya ce za a yi amfani da bashin ne domin fadada wani shirin samar da walwalar jama’a musamman talakawa da gajiyayyu a fadin Nijeriya.
Shugaba Miuhammadu Buhari ya ce, za a ciyo sabon bashin ne daga Bankin Duniya.
Wannan dai ya na zuwa ne, a daidai lokacin da shugaba Buhari ke shirin mika mulki ga zababben shugaban kasa Bola Ahmed Tinubu .