Site icon Liberty TV/Radio Hausa – Labaru – Tashar 'Yanci!

APC Ta Yi Allah Wadai Da Rusau Ɗin Gwamnatin Abba A Kano

Jam’iyyar APC a jihar Kano, ta yi Allah wadai da rushe-
rushen da gwanmnatin Abba Kabir Yusuf ta ke yi, lamarin da
ta bayyana a matsayin farmaki a kan dukiyoyin al’umma.

A cikin wata sanarwa da muƙaddashin shugaban jam’iyyar na jihar Kano Shehu Maigari ya raba wa manema labarai, APC ta ce a yau Kano ta kasance abin tausayi saboda halin da jam’iyyar NNPP ta jefa ta a ciki, inda ta zargi NNPP da gwamnatin Abba Gida-Gida da jefa ‘yan kasuwa cikin mawuyacin hali.

Ta ce matakin da NNPP ta ɗauka na rusa wasu wuraren kasuwanci a jihar ya sa wasu matasa sun zama ɓarayi saboda su na yawo da makamai tare da fasa shagunan mutane domin satar kaya.

A karshe ta yi kira ga iyayen yara, musamman matasan da ta ce gwamnatin NNPP ta na amfani da su wajen ɓarnata kayan al’umma su ja kunnen ‘ya’yan su.

Exit mobile version