Site icon Liberty TV/Radio Hausa – Labaru – Tashar 'Yanci!

‘Yan Gudun Hijira: Shettima Ya Nemi Hadin Kan Kasashen Duniya

VP Shettima4 e1689963604715

VP Shettima4 e1689963604715

Mataimakin shugaban Najeriya, Shettima, ya yi kira ga kawayen Najeriya su hada kai domin magance matsalar ‘yan gudun hijira.


ya yi kiran ne a wani taron kaddamar da tsare-tsare na jihohi kan magance matsugunin cikin gida da za a aiwatar a jihohin Arewa guda hudu,

mataimakin shugaban kasan ya bayyana dabarun da gwamnatin shugaba Bola Tinubu ta dauka wajen tunkarar kalubalen ‘yan gudun hijira a Najeriya,


inda ya ce gwamnati na ba da fifiko ga rayuwar al’ummar ta musamman a wannan mawuyacin lokaci.


Ya kuma yi alkawarin cewa gwamnatin tarayya za ta himmatu wajen tabbatar da lafiyar da walwalar ‘yan gudun hijira a
Najeriya.


Shirin ya samo asali ne daga babban Sakatare Janar na Majalisar Ɗinkin Duniya ya tsara kan ƙaura Ndaga matsugunai

wanda ke da nufin taimakawa mutanen da ke gudun hijira a cikin gida su sami mafita mai ɗorewa.

Exit mobile version