Site icon Liberty TV/Radio Hausa – Labaru – Tashar 'Yanci!

‘Yan Daba Sun Tayar Da Rikici Saboda Dokar Hana Fita

‘Yan Daba Sun Tayar Da Rikici Saboda Dokar Hana Fita

‘Yan Daba Sun Tayar Da Rikici Saboda Dokar Hana Fita

Hatsaniya ta barke a wasu sassam Jihar Legas biyo bayan tsaiwaita dokar zaman gida da Gwamantin Tarayya ta yi a jihohin Legas da Ogun da kuma Abuja.

Shugaban kasa Muhammadu Buhari ya sanar da tsawaita dokar ne  domin hana yaduwar cutar COVID-19 a jihohin, matakin da bai yi wa wasu mazuna yakin Legas dadi ba.

Wasu fustattun matasa fiye da 100, dauke da makamai sun yi ta shiga unguwanni a jihar Legas inda suka rika huce fushinsu a kan mutanan da ba su ji ba su gani ba.

Ta’adin na daren Litinin ya yi kama da abin da ya auku a ranar Lahadi, inda da tsakar rana ‘yan daba suka rika yi wa jama’a kwace, tare fasa shaguna da gidajen suna kwasan kaya a jihohin Legas da Ogun.

Ta’addancin ‘yan daban dauke da makamai ya tayar da hankulan mazauna yankunan Mangoro da Ogba da Agege da Iyana Ipaja da kuma Dopemu. 


Exit mobile version