Site icon Liberty TV/Radio Hausa – Labaru – Tashar 'Yanci!

Wazirin Katsina Ya Yi Murabus Daga Kan Kujerar Sa

Wazirin Katsina Farfesa Sani Abubakar Lugga, ya yi murabus daga majalisar masarautar Katsina, biyo bayan tuhumar da majalisar ta yi ma shi cewa ya tattauna batutuwan rashin tsaro a birnin Ilorin na jihar Kwara ba tare da yardar masarautar ba.

A ranar 14 ga watan Fabrairu ne Farfesa Lugga ya halarci wani taro a Ilorin, inda ya ce yawan hare-haren ‘yan bindiga sun yi sanadiyar rufe makarantu a kananan hukumomi takwas na jihar Katsina.

Farfesa Lugga, ya ce lamarin ya kai ga har hakiman kananan hukumomin takwas sun koma cikin birnin Katsina da zama sakamakon hare-haren, sai dai hakan bai yi wa majalisar masarautar Katsina dadi ba, inda ta aike ma shi da tuhuma.

Yayin da ya ke martani a kan tuhumar, Farfesan ya amsa lamurra uku da majalisar ke tuhumar sa a kai, sannan daga bisani ya gabatar wa Mai Martaba Sarkin Katsina Alhaji Abdulmumini Kabir Usman takardar ajiye sarautar sa.

Exit mobile version