Ministan Shari’a Abubakar Malami, ya aike wa shugaba Muhammadu Buhari wasikar neman ya tsige shugaban hukumar yaki da cin hanci da rashawa EFCC Ibrahim Magu, bisa wasu zarge-zargen rashawa akalla 20.
Wata majiya ta ce daga cikin zarge-zargen da Ministan ya yi wa Ibrahim Magu, akwai zargin karkatar da kudaden sata, sannan ba ya da biyayya ga na gaba da shi a gwamnati.
Majiyoyi fda dama sun ruwaito cewa, Malami ya bada jerin sunayen mutane uku da za a maye Ibrahim Magu da su, amma magoya bayan Magu da ke fadar shugaban kasa na cewa, cire Magu a wannan lokacin na iya zama babban kuskure.
Majiyoyin sun ce, abin takaici ne a ce Magu ya na fuskantar wasu miyagu da su ka rantse sai sun cire shi duk da nasarorin da ya samu, sai dai sun ce duba ga irin tuhume-tuhumen da ake yi wa ma shi, akwai yiwuwar shugaba Buhari ya bukaci kafa kwamitin bincike kafin ya yanke shawara.