Tawagar Gwamnatin tarayya ƙarkashin jagorancin Shugaban kamfanin man fetur na Najeriya NNPC Mele Kyari ta isa Senegal domin ta’aziyyar rasuwar jagoran Dariƙar Tijjaniya a Afrika wato Sheik Khalifa Ahmed Tijjani Inyass.
A wani saƙo da mai ba shugaban ƙasa shawara kan kafofin yada labarai na zamani Bashir Ahmed, ya wallafa a shafin sa na Twitter, ya bayyana cewa cikin waɗanda suka je ƙasar yin ta’aziyyar amadadin Shugaba Buhari, akwai Shugaban hukumar kula da shige da fice ta Najeriya Muhammed Babandede.
A wannan makon ne dai Marigayi Sheik Khalifa Ahmed Tijjani Inyass, ya rasu, kuma tuni aka yi jana’izar sa a birnin Kaulaha da ke ƙasar ta Senegal.