Site icon Liberty TV/Radio Hausa – Labaru – Tashar 'Yanci!

Ta’aziyya: Tawagar Da Shugaba Buhari Ya Aika Ta Isa Senegal

Gwamnati Ba Ta Cire Dokar Hana Zirga-Zirga A Tsakanin Jihohi Ba

Gwamnatin Tarayya ta fara aikin sake gina makarantun da Boko Haram su ka ragargaza a Jihar Yobe da sauran sassan jihohin Arewa maso Gabas.

Tawagar Gwamnatin tarayya ƙarkashin jagorancin Shugaban kamfanin man fetur na Najeriya NNPC Mele Kyari ta isa Senegal domin ta’aziyyar rasuwar jagoran Dariƙar Tijjaniya a Afrika wato Sheik Khalifa Ahmed Tijjani Inyass.

A wani saƙo da mai ba shugaban ƙasa shawara kan kafofin yada labarai na zamani Bashir Ahmed, ya wallafa a shafin sa na Twitter, ya bayyana cewa cikin waɗanda suka je ƙasar yin ta’aziyyar amadadin Shugaba Buhari, akwai Shugaban hukumar kula da shige da fice ta Najeriya Muhammed Babandede.

A wannan makon ne dai Marigayi Sheik Khalifa Ahmed Tijjani Inyass, ya rasu, kuma tuni aka yi jana’izar sa a birnin Kaulaha da ke ƙasar ta Senegal.

Exit mobile version