Site icon Liberty TV/Radio Hausa – Labaru – Tashar 'Yanci!

Majalisa Za Ta Binciki Zargin Badakala Naira Biliyan 40 A Hukumar NDDC

Majalisa Za Ta Binciki Zargin Badakala Naira Biliyan 40 A Hukumr NCDC

Majalisa Za Ta Binciki Zargin Badakala Naira Biliyan 40 A Hukumr NCDC

Majalisar wakilai za ta fara bincike a kan zargin da ake yi na cewa, an tafka badakala a hukumar kula da cigaban yakin Neja delta NDDC.

Kawo yanzu dai, majalisar ta aikawa ministan harkokin Neja-Delta, Godswill Akpabio da ‘yan kwamitin rikon kwaryar hukumar takarda gayyata domin amsa wasu tambayoyi a majalisar.

Majalisar wakilai dai, t na zargin an wawuri wasu makudan kudade a hukumar NDDC, wacce take karkashin kulawar sanata Godswill Akpabio.

Haka kuma, majalisar ta bukaci kwamitin da ke sa ido a kan harkokin Neja-Delta ya binciki zargin karkatar da Naira biliyan 40 da aka ce an kashe a cikin watanni biyu zuwa uku, tare da gabatar da  rahoton binciken a kan lokaci.

‘Yan majalisar sun cimma wannan matsaya ne bayan dan majalisa Peter Akpatason ya kawo da kudirin a zaman majalisar na ranar talatar da ta gabata.

A karshe majalisar ta yanke hukuncin kiran Godswill Akpabio da shugabannin hukumar NDDC na rikon kwarya domin su yi wa ‘yan Nijeriya bayanin aikin da su ke yi da kudaden.

Exit mobile version