Site icon Liberty TV/Radio Hausa – Labaru – Tashar 'Yanci!

Kotun Daukaka Kara Ta Kori Dan Majalisar Alhassan Ado Doguwa

Alhassan Ado Doguwa

Kotun daukaka kara da ke zama a Kaduna, ta kori dan majalisa mai wakiltar mazabar Tudun Wada da Doguwa ta jihar Kano kuma shugaban masu rinjaye a majalisar wakilai Alhassan Ado Doguwa.

Ado Doguwa dais hi ne mutum mafi girman kujera na uku a majalisa bayan shugaban majalisa da mataimakin sa.

Kotun, ta yi watsi da zaben kananan hukumomi biyu da Ado Doguwa ke wakilta bisa zargin magudin da aka tafka a zaben watan Febrairu na shekara ta 2019.

Alkalan kotun, a karkashin jagorancin mai shari’a Oludotun Adefope-Okojie, sun yi ittifakin cewa ba zai yiwu a amince da sakamakon zaben ba, saboda babu sunayen wasu ‘yan takara a takardar sakamakon da hukumar zabe ta sanar.

Kotun, ta ce hukumar zabe ta tafka babban kuskuren rubuta sakamakon jam’iyyu biyu kadai daga cikin 53 da su ka yi takara.

Exit mobile version