An yi wa ‘yan Nijeriya mazauna kasar Afirka ta Kudu tayin jirgin sama kyauta domin dawowa gida, bayan barkewar rikice-rikicen nuna kin jinin baki kamar yadda ma’aikatar harkokin kasashen wajen Nijeriya ta bayyana.
Ma’aikatar ta ce, mamallakin kamfanin jiragen sama na Air Peace ya ce zai bada jirgi kyauta a kwaso ‘yan Nijeriya aranar Juma’a mai zuwa.
A cikin wata sanarwa da ma’aikatar ta fitar, ta ce ‘yan Nijeriya da ke sha’awar dawowa gida na iya tuntubar ofishin jakadancin Nijeria a biranen Pretoria da Johannesburg domin shirye-shiryen da su ka dace.
Harin da aka kai wa shaguna da wuraren sana’a na baki a kasar Afirka ta Kudu dai ya tunzura ‘yan Nijeriya da dama da ke ganin ba a yi adalci ba.
Ministan harkokin wajen Nijeriya Geoffrey Onyeama ya shaida wa manema labarai cewa, bayanan da ya samu sun nuna cewa ba a kashe dan Nijeriya ko guda a rikicin ba.