Rundunar yan sandan Nijeriya ta harba barkono mai sa hawaye a dandazon wasu mutane ka suka yi cincirindo a kafar shiga a majalisar dokokin jihar Yobe.
Lamarin dai ya faru ne ne jim kadan bayan gwamnan jihar Mai Mala Buni ya shiga zauren majalisar domin gabata da kasafin kudin shekara ta 2020 a gaban majalisar.
Bayan
isowar gwamnan majalisar dai, sai ‘yan sandan su ka gaza dai-dai-ta dandazon mutanan
da su ka rako gwamnan, lamarin da ya sa suka harba barkonon tsohuwa domin
tarwatsa dandazon mutanan.