Site icon Liberty TV/Radio Hausa – Labaru – Tashar 'Yanci!

Joe Biden Na Ci Gaba Da Samun Nasara

Joe Biden Na Ci Gaba Da Samun Nasara

Joe Biden Na Ci Gaba Da Samun Nasara

Tsohon Mataimakin shugaban Amurka Joe Biden ya sake samun gagarumar nasara a zaben fidda gwanin Jam’iyyar Democrat da aka yi a ranar talata a Jihohi 6, matakin da ya say a zamo a sahun gaba wajen kayar da Sanata Bernie Sanders domin kalubalantar shugaba Donald Trump a zaben watan Nuwamba.

Manazarta na ci gaba da bayyana cewa, Joe Biden ya lashe jihohi 9 daga cikin jihohi 14 da suka kada kuri’a a zaben Super Tuesday, domin fida dan takara a Jam’iyyar Democrat.

Biden ya bada mamaki ganin yadda ya sha gaban babban abokin takarar sa, Bernie Sanders a jihar Texas mai muhimmanci, sai dai ana hasashen cewa, Mr Sanders zai yi nasara a California da kuma wasu karin jihohi uku.

‘Yan takarar biyu na kan gaba wajen neman tikitin fafatawa da shugaba Donald Trump a zaben shugaban kasa da za a gudanar a watan Nuwamba mai zuwa.

Tsohon Magajin Garin Birnin New York, Michael Bloomberg ya kashe fiye da rabin Dala biliyan 1 a yakin neman zaben sa, amma bai lashe koda jiha daya ba.

Exit mobile version